Mika6hau_bib

Damuwar Ubangiji a kan Isra’ila

1Ku saurari abin da Ubangiji ya ce,“Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu;bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
2“Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku,ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya.Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa;yana tuhumar Isra’ila.
3“Ya ku mutanena, me na yi muku?Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.4Na fito da ku daga ƙasar Masarna kuma ’yantar da ku daga ƙasar bauta.Na aika da Musa yă jagorance ku,haka ma Haruna da Miriyam.5Ya ku mutanena, ku tunaabin da Balak sarkin Mowab ya ƙullada kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar.Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal,don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
6Da me zan zo a gaban Ubangijiin rusuna a gaban Maɗaukaki Allah?Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa,da ɗan maraƙi bana ɗaya?7Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbaida kuma rafuffukan mai dubbai goma?Zan ba da ɗan farina ne don laifina,ko ’ya’yan jikina domin zunubin raina?8Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau.Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwashi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙaika kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.

Laifin Isra’ila da kuma hukunci

9Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni,a ji tsoron sunana kuwa hikima ce,“Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.10Har yanzu zan manta, ya muguwar gidada dukiyarki da kika samu a muguwar hanyazan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?11Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya,da kuma buhun ma’aunan ƙarya?12Attajiranta masu fitina ne;mutanenta kuma maƙaryata neharsunansu kuwa suna yaudara.13Saboda haka, zan hallaka kuin lalace ku saboda zunubanku.14Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba,cikinku zai zama babu komeZa ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba,gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.15Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba;za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba,za ku tattaka ’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.16Kuna kiyaye ƙa’idodin Omrida dukan ayyukan gidan Ahabkun kuma bi al’adunsu.Saboda haka, zan maishe ku kufaiin mai da ku abin dariya a cikin mutane,za ku sha reni a wurin al’ummai.”