Mika1hau_bib

1Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
2Ku ji, ya ku mutane duka,ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki,bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku,daga haikalinsa mai tsarki.

Hukunci a kan Samariya da kuma Urushalima

3Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa;zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.4Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa,kamar kaki a gaban wuta,kwaruruka kuma za su ɓace,kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.5Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub,da kuma zunuban gidan Isra’ila ne.Mene ne laifin Yaƙub?Shin, ba Samariya ba ce?Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda?Shin, ba Urushalima ba ce?
6“Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji,wurin noman inabi.Zan zubar da duwatsunta a cikin kwariin kuma bar harsashin gininta a bayyane.7Za a ragargaje dukan allolinta;za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta;zan lalatar da dukan gumakanta.Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su,ga karuwanci kuma za su koma.”

Kuka da Makoki

8Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka;zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara.Zan yi kuka kamar dila,in yi baƙin ciki kamar mujiya.9Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne;ya bazu har Yahuda.Ya ma kai bakin ƙofar mutanena,har ma Urushalima da kanta.10Kada a faɗe shi a Gat;kada ma a yi kuka.A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙuraa Bet-Leyafra .11Ku wuce tsirara da kuma kunya,ku mazaunan Shafir .Bet-Ezel tana makokidomin babu wani daga Za’ananda ya fito don yă taimaka.12Mazaunan Marotsun ƙosa su ga alheri,amma Ubangiji ya sauko da azaba,har zuwa ƙofar Urushalima.13Ku da kuke zama a Lakish,ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi.Gama ku kuka fara yin zunubia Sihiyona,gama an sami laifofin Isra’ilaa cikinku.14Saboda haka za ku ba da kyautan bankwanaga Moreshet Gat.Garin Akzib zai zama abin yaudaraga sarakunan Isra’ila.15Ku mazaunan MareshaUbangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi.Sarakunan Isra’ilaza su gudu zuwa Adullam.16Ku aske kanku ƙwal don makoki,ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu.Gama za a ja ’ya’yan da kuke farin cikia kai su bauta.