Zefaniya2hau_bib

1Ku tattaru, ku tattaru,Ya ku al’umma marar kunya,2kafin ƙayyadadden lokacin nan yă zoranan nan kuma ta share ku kamar ƙaiƙayikuma kafin fushi mai tsanani na Ubangiji yă auko muku,kafin ranar fushin Ubangiji ta auko muku.3Ku nemi Ubangiji, dukanku ƙasashe masu tawali’u,ku da kuke yin abin da ya umarta.Ku nemi adalci da tawali’u;mai yiwuwa ku sami mafaka a ranar fushin Ubangiji.

Hukunci a kan Filistiya

4Za a yashe Gazaa kuma bar Ashkelon kango.Da tsakar rana Ashdod za tă zama babu kowaa kuma tumɓuke Ekron.5Taku ta ƙare ku da kuke zama a bakin teku,Ya ku mutanen Keretawa;maganar Ubangiji tana gāba da ke,Ya ke Kan’ana, ƙasar Filistiyawa.“Zan hallaka kikuma babu abin da zai rage.”6Ƙasar da take a bakin teku, inda Keretawa suke zaune,za tă zama wurin da makiyaya da ta garken tumaki.7Za tă zama mallakar raguwar gidan Yahuda;a can za su sami wurin kiwo.Da yamma za su kwantaa gidajen Ashkelon.Ubangiji Allahnsu zai lura da su;zai maido musu da martabarsu.

Hukunci a kan Mowab da Ammon

8“Na ji irin zagin da Mowab take yi,da kuma ba’ar Ammonawa,waɗanda suka zagi mutanenasuna kuma yi barazana a kan ƙasarsu.9Saboda haka, muddin ina raye,”in ji Ubangiji Maɗaukaki,Allah na Isra’ila,“tabbatacce Mowab za tă zama kamar Sodom,Ammonawa kuma kamar Gomorra,ƙasa mai ciyayi da rammukan gishiri,ƙasa marar amfani har abada.Raguwar mutanena za su washe su;waɗanda suka rage na al’ummata za su gāda ƙasarsu.”
10Wannan ne zai zama sakamakon girmankansu,saboda zagi da kuma ba’ar da suka yi wa mutanen Ubangiji Maɗaukaki.11Ubangiji zai zama abin tsoro a gare susa’ad da ya hallaka allolin ƙasar.Al’ummai a kowane bakin teku za su yi masa sujada,kowa a ƙasarsa.

Hukunci a kan Kush

12“Ku ma, ya Kushawa,za a kashe ku da takobina.”

Hukunci a kan Assuriya

13Zai kuma miƙa hannunsa gāba da arewayă kuma hallaka Assuriya,zai mai da Ninebe kango gaba ɗayata kuma zama busasshiya kamar hamada.14Garkuna za su kwanta a can,da kowace irin halitta,Mujiyar hamada da bushiyaza su zauna a kan ginshiƙanta.Kukansu za tă ratsa tagogi,ɓuraguzai za su tare ƙofofin shiga,za a kware ginshiƙan al’ul.15Birnin da yake harka ke nanda take zaune lafiya.Ta ce wa kanta,“Ni ce, kuma babu kamata.”Dubi irin kangon da ta zama mana,mazaunin namun jeji!Duk wanda ya wuce ta sai ya yi mata tsakiyana kaɗa kai.