ROM15hau_bib
1Mu da muke da ƙarfi ya kamata mu yi haƙuri da kāsawar marasa ƙarfi ba kawai mu gamshi kanmu ba.2Ya kamata kowannenmu yă faranta wa maƙwabcinsa rai don kyautata zamansa domin kuma yă gina shi.3Gama ko Kiristi ma bai gamshi kansa ba, amma kamar yadda yake a rubuce cewa, “Zage-zagen da waɗansu suka yi maka, duk sun fāɗo a kaina.”4Gama duk abin da aka rubuta a dā an rubuta ne domin yă koya mana, don ta wurin jimrewa da kuma ƙarfafawar Nassosi mu kasance da bege.5Bari Allah mai ba da haƙuri da kuma ƙarfafawa yă ba ku ruhun haɗinkai da juna yayinda kuke bin Kiristi Yesu,6don da zuciya ɗaya da kuma baki ɗaya kuke ɗaukaka Allah da kuma Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi.7Ta haka sai ku karɓi juna kamar yadda Kiristi ya karɓe ku, don a yabi Allah.8Ina dai gaya muku cewa Kiristi ya zama bawan Yahudawa a madadin gaskiyar Allah, don yă tabbatar da alkawaran da aka yi wa kakannin kakanninmu9domin Al’ummai su ɗaukaka Allah saboda jinƙansa, kamar yadda yake a rubuce,“Saboda haka zan yabe ka a cikin Al’ummai;zan rera waƙoƙi ga sunanka.”10Ya kuma ce,“Ku yi farin ciki, ya Al’ummai, tare da mutanensa.”11Da kuma,“Ku yabi Ubangiji, dukanku Al’ummai,ku kuma rera masa yabo, dukanku mutanen duniya.”12Kuma Ishaya ya ce,“Tushen Yesse zai tsiro,wanda zai taso yă yi mulkin al’ummai;al’ummai za su sa bege a gare shi.”13Bari Allah na bege yă cika ku da matuƙar farin ciki da salama yayinda kuke dogara gare shi, domin ku yalwata cikin bege ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.