Zabura42hau_bib

Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskilne na ’Ya’yan Kora maza.

1Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka,haka raina yake marmarinka, ya Allah.2Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai.Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?3Hawayena ne sun zama abincinadare da rana,yayinda mutane suke ce da ni dukan yini,“Ina Allahnka ɗin?”4Waɗannan abubuwa ne nakan tunasa’ad da nake faɗin abin da yake a raina,yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a,ina bishe su a jere zuwa gidan Allah,da sowa ta farin ciki da kuma godiyaa cikin taron biki.
5Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina?Me ya sa ka damu a cikina?Ka dogara ga Allah,gama zai sāke yabe shi,Mai Cetona da kuma Allahna.
6Raina yana baƙin ciki a cikina;saboda haka zan tuna da kaidaga ƙasar Urdun,a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.7Zurfi kan kira zurficikin rurin matsirgar ruwanka;dukan raƙuma da igiyoyisun sha kaina.
8Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa,da dare waƙarsa tana tare da ni,addu’a ga Allah na raina.
9Na ce wa Allah Dutsena,“Me ya sa ka manta da ni?Me zai sa in yi ta yawo ina makoki,a danne a hannun abokin gāba?”10Ƙasusuwana suna jin jiki da wahalayayinda maƙiyana suna mini ba’a,suna ce mini dukan yini,“Ina Allahnka ɗin?”
11Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina?Me ya sa ka damu a cikina?Ka dogara ga Allah,gama zai sāke yabe shi,Mai Cetona da kuma Allahna.