Zabura124hau_bib

Waƙar haurawa. Ta Dawuda.

1Da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu ba,bari Isra’ila yă ce,2da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu basa’ad da aka auka mana,3sa’ad da fushinsu ya ƙuna a kanmu,ai, da sun haɗiye mu da rai;4da rigyawa ta kwashe mu,da ambaliya ta rufe mu.5Da ruwa mai haukaya share mu ƙaf.
6Yabo ya tabbata ga Ubangiji,wanda bai bari aka yayyage mu da haƙoransu ba.7Mun tsira kamar tsuntsudaga tarkon mai farauta;an tsinke tarko,muka kuwa tsira.8Taimakonmu yana a sunan Ubangiji,Wanda ya yi sama da ƙasa.