Ishaya23hau_bib

Annabci a kan Taya

1Abin da Allah ya faɗa game da Taya.Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish!Gama an hallaka Tayaaka kuma bar su babu gida ko tasha.Daga ƙasar Saifurusmagana ta zo musu.
2Ku yi shiru, ku mutanen tsibirida ku ’yan kasuwan Sidonwaɗanda masu ciniki a teku suka azurta.3A manyan ruwayehatsin Shihor suka iso;girbin Nilu ne kuɗin shiga na Tayata kuma zama kasuwar al’ummai.
4Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku,gama teku ya yi magana ya ce,“Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi ’ya’ya;ban taɓa goyon ’ya’ya maza ba balle in reno ’ya’ya mata.”5Sa’ad da magana ta kai Masar,za su razana da jin labari daga Taya.
6Ku haye zuwa Tarshish;ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.7Wannan ce birnin murnanku,birnin nan na tun dāwadda ƙafafunta suka kai tazama a ƙasashe masu nesa?8Wane ne ya ƙulla wannan a kan Tayaita da take ba da rawanin sarauta,wadda ’yan kasuwanta sarakuna ne,wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?9Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi,don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajartaya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
10Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu,Ya Diyar Tarshish,gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.11Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa tekuya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki.Ya ba da umarni game da Funisiyacewa a hallaka kagararta.12Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba,Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya!“Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus;a can ɗin ma ba za ki huta ba.”13Dubi ƙasar Babiloniyawa,wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani!Assuriyawa sun mai da itawurin zaman halittun hamada;sun gina hasumiyoyin kwanto,suka ragargaza kagararta ƙafsuka mai da ita kango.
14Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish;an rurrushe kagararku!15A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,16“Ɗauki garaya, ki ratsa birni,Ya ke karuwar da aka manta da ita;kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa,saboda a tuna da ke.”17A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.18Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.