Amos2hau_bib
1Ga abin da Ubangiji ya ce,“Saboda zunubai uku na Mowab,har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba.Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edomsuka zama sai ka ce toka.2Zan sa wuta a Mowabda za tă ƙone kagarun KeriyotMowab za tă gangara cikin hayaniya mai girmacikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.3Zan hallaka mai mulkintazan kuma kashe shugabanninta.”4Ga abin da Ubangiji ya ce,“Saboda zunubai uku na Yahuda,har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba.Gama sun ƙi bin dokar Ubangijiba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba,domin allolin ƙarya sun ruɗe su,allolin da kakanninsu suka bauta.5Zan sa wuta a Yahudada za tă ƙone kagarun Urushalima.”